Shugaban Yan majalisun Arewacin Nijeriya Rt Hon Alhassan Ado Doguwa sardaunan kasar hausa Mai tuta (OON) ya Tallafawa mutanen Garuruwan da suka hada da Bahawa da Ririwai da Asada da makamantansu, bisa yadda iftila, in guguwa da Ruwa da Tsawa ya afka a yankin.
Cikin wata sanarwa da Mai magana da yawun Rt Hon Alhassan Ado Doguwa ya fitar Auwal Ali Sufi utai, yace Hon Alhassan Ado Doguwa ya bada tallafin fiye da Naira Miliyan 10, a baya sakamakon yadda iftila, in ya yawaita ne yasa Hon Alhassan Ado ya kafa kwamiti karkashin jagorancin tsohon kwamishina Alh musa Salihu Ririwai, tare da wasu mahimman mutane, kana suka sa aka akayi bibiyar yadda AL, amarin ya kasance,.
Hon Alhassan Ado ya bada tallafin ne a Dakin taro na multipurpose dake yankin karamar hukumar Doguwa, Yayinda aka tara dukkan wadanda suka, samu wannan jarabta, aka gudanar da Addu’oi, dan kare afkuwar hakan.

Duk da haka dai Hon Alhassan ya bada tallafi na naira miliyan 10, yayin da sanata kawu sumaila ya bada Naira miliyan 10 kana Yan majalisun tudun wada da Doguwa a majalisar Jihar kano Hon sule shuwaki da Hon Salis Ibrahim Muhammad jikan Liman suka bada naira miliyan daya kowannensu.
Daga bisani hukumar dake bada Agajin gaggawa ta kasa (NEMA) itama ta bada tallafin Kayayyakin Abinci da suturu domin rage radadin iftila, in
Daga bisani an bukaci wadanda suka Amfana da tallafin da suyi Amfani dashi ta hanyar data dace.

