Tun da farko dai Ibrahim Shitu Canji shine ya fara tabbatar wa da Hikima Radio batun ajiye aikin, daga bisani ƙungiyar ta sanar da ajiye aikin a hukumance.

Ƙungiyar ta ƙara sanar da raba gari da mai horas da ita Ladan Bosso.

Wata majiya tace an daɗe ana tattaunawa domin a samu daidaito tsakanin Ibrahim Canji da mai ƙungiyar wato Sanata Barau, kafin a cimma daidaiton biyan tsohon shugaban haƙƙinsa.

Kawo yanzu dai ana dakon sabuwar sanarwa daga ƙungiyar Barau FC na waɗanda za su jagorance ta.

Mai zaku ce dangane da wannan lamari??

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version