Close Menu
  • Home
  • Kasuwanci
  • Nishadi
  • Features
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Karin Wasu
    • Noma da Kiwo
    • Sauyin Yanayi
    • Fasaha
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) Instagram
MURYAR AREWA A YAU
Subscribe
  • Home
  • Kasuwanci

    GWAMNAN JIHAR KANO ALH ABBA KABIR YUSUF YA SAUKE KWAMISHINAN ZUBA JARI DA KASUWANCI, DAGA KAN MUKAMINSA

    March 26, 2026

    FILIN JIRGIN SAMAN DUTSE JIHAR JIGAWA ZAI DINGA KARBAR KAYA NA KAGO

    February 23, 2026

    Zulum Leads Fintiri, Buni to Meet New World Bank Director

    November 14, 2025

    Gwamnatin Najeriya ta roki jama’a su rage cin ganda (ponmo) kada kamfanin sarrafa fata na kasar ya durkushe

    November 14, 2025

    STANDARD ORGANIZATION OF NIGERIA AND FEDERAL MINISTRY OF TRADE ARE GOING TO WORK TOGETHER

    November 8, 2025
  • Nishadi

    WANI : MAGIDANCI MAI MATA BIYU A BAUCHI, YA KASHE DAN ACABA DON SAMUN KUDIN KARA AUREN MATA TA UKU

    October 22, 2025

    Qausain TV appoints Adam A. Zango as Director-General

    October 8, 2024

    Young Jonn Sets To Thrill Fans With Electrifying Performance In Abuja

    September 29, 2024

    Why Bobrisky was separated from other inmates – Prison experts

    September 27, 2024
  • Features

    ANKARAWA SARAKUNAN GARGAJIYA ALBASHI DA KIMANIN KASHI 300

    May 26, 2026

    KUNGIYAR YAN JARIDU TA KASA RESHEN JIHAR JIGAWA TA RABA KUDADE GA YAYAN KUNGIYAR DOMIN GUDANAR DA SHAGULGULAN SALLAH BABBA

    May 26, 2026

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA TARE DA HADIN GWIWAR AFRICAN PERINATAL SOCIETY ZASU INGANTA HARKOKIN LAFIYA TUN DAGA TUSHE

    May 25, 2026

    TSOHON DAN MAJALISAR WAKILAI NA TARAYYA YA KOMA JAM, IYYAR NDC, WAJEN SANATA KWANKWASO

    May 25, 2026

    KANO STATE SSG, DG NPC BAFFA DAN’AGUNDI , COMMISSIONERS , SPECIAL l ADVISERS TO PLAN 3-YEAR ANNIVERSARY y OF f GOV . ABBA KABIR YUSUF f

    May 24, 2026
  • Labarai

    SHUGABAN NIJERIYA BOLA AHMED TINUBU YA SANYA HANNU AKAN KASAFIN KUDI NA SHEKARA TA 2026 DA TSAWAITA DOKAR KASAFIN KUDI TA SHEKARA TA 2025

    April 18, 2026

    ALLAH YA YIWA MAHAIFIYAR HON IBRAHIM UMAR BALLAH RASUWA

    April 17, 2026

    JIGAWA A ROLE MODEL FOR HEALTH SECTOR REFORMS IN NIGERIA – ZAMFARA PS PUBLIC SERVICE OFFICE

    April 1, 2026

    AN TSARE WANI DIREBAN MOTAR MATAR SARKI BISA ZARGIN SATAR GWALA – GWALAI NA MILIYOYIN KUDI MASU TSADAR GASKE

    April 1, 2026

    CELEBRATING A VISIONARY LEADER r AT 74TH : DG DAN’AGUNDI FELICITATES PRESIDENT TINUBU ON HIS BIRTHDAY

    March 29, 2026
  • Siyasa

    HON DOGUWA YA ROKI AFUWAR GWAMNAN JIHAR KANO, BISA MAKAUNIYAR ADAWA DA MUKAYI MASA

    May 19, 2026

    WANI MATASHI MAI SUNA UMAR UZAIRU DIREBA YA SAUYA SHEKA ZUWA JAM, IYYAR APC BAYANDA YA BAYYANA JAM, IYYAR DA CEWAR ITACE MAFITA A ZABEN 2027

    April 21, 2026

    GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI DAN MODI YA KADDAMAR DA KWAMITIN WAYAR DA KAI

    April 20, 2026

    REJOINDER: THE FALLACY OF THE “COMMANDER AND THE BURDEN OF INTEGRITY

    April 5, 2026

    MATASAN JIHAR KANO SUNCE :-MURTALA SULE GARO NE YAFI CANCANTAR ZAMA MATAIMAKIN GWAMNAN JIHAR KANO

    April 4, 2026
  • Tsaro

    JIGAWA STATE IS A WRONG PLACE TO COMMIT CRIME AS AFFIRMED BY THE DECISIONS OF THE SUPREME COURT OF NIGERIA.

    April 11, 2026

    YAN FASHIN DAJI NA FAMA DA ANNOBAR AMAI DA GUDAWA, HAR TA YI AWON GABA DA WASU DAGA CIKIN SU ZUWA LAHIRA

    April 9, 2026

    KHADIJA ISAH THE 9 YEAR OLD VICTIM OF BRUTAL RAPE GOT JUSTICE .

    April 9, 2026

    GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI DAN MODI YA YI WA WASU MASU ZAMAN GIDAN GYARAN HALI AFUWA 12

    March 19, 2026

    GWAMNATIN JIHAR KANO TA DAUKI MATAKIN TSAURARA TSARO YAYIN SALLAR IDI DA ZA, A GABATAR NAN GABA KADAN DOMIN BIN DOKA DA ODA

    March 18, 2026
  • Wasanni

    Ndume Unity Cup 2025: Drama, Determination, and Dominance as Matchday 1 Unfolds.

    November 15, 2025

    MAGOYA BAYAN KUNGIYAR KWALLON KAFA TA KATSINA UNITED TA SUN RAUNATA YAN WASAN KUNGIYAR KWALLON KAFA TA BARAU FC TARE DA YIWA MOTOCIN BARAU FC ROTSE

    November 8, 2025

    NASARAR GIWA UNITED FILIN SUKUWA

    October 24, 2025

    new Kano-based football club, Bichi First FC, has appointed renowned journalist Muzammil Dalha Yola as its Media Officer.

    September 12, 2025

    Kungiyoyin Kwallon Kafa Na Barau da Kano pillars Duk Na Y’aya”n Jihar kano ne Ba Na Mutum Daya bane – :Inji Adamu Abdullahi karkasara

    August 19, 2025
  • Karin Wasu
    1. Noma da Kiwo
    2. Sauyin Yanayi
    3. Fasaha
    4. View All

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA ZATA BULLO DA SABBIN DABARUN WARWARE MATSALOLIN MANOMA DA MAKIYAYA,TARE DA TANTANCE KAN IYAKOKI

    April 14, 2026

    GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI YA YI ALKAWARIN CI GABA DA TAIMAKA WA MANOMA DA BUNKASA TATTALIN ARZIKI

    March 22, 2026

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA TA KADDAMAR DA KASHI NA UKU NA TALLAFAWA MA, AIKATAN GWAMNATI TA FUSKAR NOMA

    March 13, 2026

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA ZATA HADA GWIWA DA NDDB NA KASAR INDIA DOMIN SAMAR DA MADARA DA BUNKASA KIWON SHANU

    March 10, 2026

    MALIKAWA GARU :- PLANT A TREE TODAY TO FIGHT DESERTIFICATION

    October 16, 2025

    Zulum commissions housing complex for teachers in Mafa

    October 7, 2025

    NiMet Predicts Three-day Thunderstorm, Downpour Nationwide

    October 14, 2024

    NiMET Predicts Three-Day Thunderstorms From Monday

    October 1, 2024

    Zulum: Borno begins export of plastic materials

    October 30, 2025

    Zamkah Technologies Has Signed MOU With Institute For Peace and Conflict Resolution (IPCR)

    September 9, 2025

    Digital Age: How Technology Impacts Modern Marriage

    September 29, 2024

    Artificial Intelligence will replace unskilled workers – Daily Trust

    September 27, 2024

    ANKARAWA SARAKUNAN GARGAJIYA ALBASHI DA KIMANIN KASHI 300

    May 26, 2026

    KUNGIYAR YAN JARIDU TA KASA RESHEN JIHAR JIGAWA TA RABA KUDADE GA YAYAN KUNGIYAR DOMIN GUDANAR DA SHAGULGULAN SALLAH BABBA

    May 26, 2026

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA TARE DA HADIN GWIWAR AFRICAN PERINATAL SOCIETY ZASU INGANTA HARKOKIN LAFIYA TUN DAGA TUSHE

    May 25, 2026

    TSOHON DAN MAJALISAR WAKILAI NA TARAYYA YA KOMA JAM, IYYAR NDC, WAJEN SANATA KWANKWASO

    May 25, 2026
MURYAR AREWA A YAU
Home » GWAMNATIN JIHAR JIGAWA TARE DA HADIN GWIWAR AFRICAN PERINATAL SOCIETY ZASU INGANTA HARKOKIN LAFIYA TUN DAGA TUSHE

GWAMNATIN JIHAR JIGAWA TARE DA HADIN GWIWAR AFRICAN PERINATAL SOCIETY ZASU INGANTA HARKOKIN LAFIYA TUN DAGA TUSHE

By Ali MuhammadMay 25, 2026 Uncategorized 4 Mins Read
IMG 20260525 WA0184
Share
Facebook Twitter Email Telegram WhatsApp

ƘUNGIYAR AFRICAN PERINATAL SOCIETY TA YABAWA CI GABAN KIWON LAFIYA A JIGAWA, TA NEMI ƘARFAFA HAƊIN GWIWA DA GWAMNATIN JIHAR

Ƙungiyar ƙwararrun likitocin kula da lafiyar mata masu juna biyu da jarirai ta Afirka, wato African Perinatal Society, ta yabawa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa gagarumin ci gaban da ta samu a fannin kiwon lafiya, musamman wajen kula da lafiyar mata masu juna biyu da jarirai, tare da neman ƙarin haɗin gwiwa da gwamnatin jihar domin ƙarfafa ingancin ayyukan kiwon lafiya.
An bayyana hakan ne yayin wata ziyarar girmamawa da tawagar shugabannin ƙungiyar ƙarƙashin jagorancin shugabanta, Farfesa Aliyu Labaran Dayyabu, suka kai wa Gwamna Malam Umar Namadi a Gidan Gwamnatin Jihar da ke Dutse.
Ziyarar ta bai wa tawagar damar sanar da gwamnan shirye-shiryen gudanar da Babban Taron Ƙasa da Ƙasa karo na biyu kan amfani da fasahar duban dan tayi (Ultrasound) da kuma lafiyar mata masu juna biyu da jarirai, tare da neman goyon baya da haɗin gwiwar gwamnatin Jigawa gabanin taron na nahiyar Afirka.
Ana sa ran gudanar da taron daga ranar 26 zuwa 28 ga watan Agustan wannan shekara, inda manyan ƙwararrun likitoci, masu bincike, ma’aikatan lafiya da masu tsara manufofi daga sassa daban-daban na Afirka za su hallara domin tattauna hanyoyin rage mace-macen mata masu juna biyu da jarirai ta hanyar bincike, kirkire-kirkire da haɗin gwiwar ƙwararru.
Da yake jawabi yayin ziyarar, Farfesa Dayyabu ya bayyana Jihar Jigawa a matsayin ɗaya daga cikin jihohin da suka yi fice wajen saka hannun jari a gine-ginen asibitoci da kuma bunƙasa ƙwararrun ma’aikatan lafiya.
Ya ce membobin ƙungiyar da suka ziyarci wasu asibitocin jihar sun gamsu da irin ci gaban da gwamnatin yanzu ta samar.
“Mun samu damar ziyartar wasu asibitoci a Jigawa kuma mun ga irin ayyukan da Mai Girma Gwamna ya yi wajen samar da ingantattun gine-gine da ɗaukar ƙwararrun ma’aikata. Wannan ne ya sa jihar ta samu nasarori wajen rage mace-macen mata masu juna biyu da jarirai, kuma muna alfahari da kasancewa tare da wannan ci gaba,” in ji shi.
Farfesa Dayyabu ya bayyana cewa an kafa African Perinatal Society ne a shekarar 2016 ƙarƙashin International Academy of Perinatal Medicine domin bunƙasa ilimin kula da lafiyar mata masu juna biyu da jarirai a Afirka ta hanyar bincike, horaswa da haɗin gwiwa.
Ya ce taken taron bana ya mayar da hankali ne kan ƙarfafa haɗin gwiwar ƙwararru domin inganta lafiyar mata da jarirai ta hanyar gano cutar hawan jini ga mata masu juna biyu (pre-eclampsia), hanyoyin kariya da magani, inganta amfani da fasahar Ultrasound, kula da haihuwa kafin lokaci, da amfani da fasahar sadarwa wajen kula da lafiya a yankunan karkara.
Haka kuma ya sanar da gwamnan shirinsu na kafa Cibiyar Bincike da Horaswa kan Lafiyar Mata da Jarirai ta Afirka, wadda za ta zama cibiyar musamman don horaswa, bincike na zamani da inganta ayyukan kula da lafiyar mata da jarirai.
Ya kuma roƙi gwamnatin Jigawa da ta tallafa wa taron tare da bai wa ma’aikatan lafiya daga jihar damar halarta.
A cewarsa, hakan zai bai wa likitoci, nas-nas, ungozomomi da sauran ma’aikatan lafiya damar samun ƙarin horo, gogewa ta ƙasa da ƙasa da kuma ƙwarewa a aikinsu.
Da yake mayar da martani, Gwamna Umar Namadi ya yi maraba da tawagar tare da yaba wa ƙungiyar bisa ƙoƙarinta na inganta lafiyar mata masu juna biyu da jarirai a faɗin nahiyar Afirka.
Ya bayyana ziyarar a matsayin mai muhimmanci, yana mai cewa haɗin gwiwa da ƙungiyoyin ƙwararru da masu bincike na da matuƙar amfani wajen magance ƙalubalen kiwon lafiya.
“Ziyararku tana da muhimmanci a gare mu saboda ku ƙwararrun ma’aikatan lafiya ne da masu bincike. A matsayinmu na gwamnati, muna buƙatar haɗin gwiwa da ƙwararru da ƙungiyoyi irin taku domin inganta harkokin kiwon lafiya a Jigawa,” in ji gwamnan.
Gwamnan ya ce mace-macen mata masu juna biyu da jarirai na ci gaba da zama babban ƙalubale a Najeriya, yana mai jaddada muhimmancin ci gaba da gudanar da bincike da tsara manufofi bisa hujjoji da ƙarfafa haɗin gwiwar ƙwararru domin rage matsalar.
Ya tabbatar wa tawagar cewa gwamnatin jihar za ta tallafa wa taron tare da ɗaukar nauyin ma’aikatan lafiya daga Ma’aikatar Lafiya da asibitocin gwamnati domin halarta.
“Muna cikakken goyon bayan manufofin wannan taro saboda mun yi imanin cewa sakamakonsa zai samar da hanyoyin da za su taimaka mana wajen ƙara inganta harkokin kiwon lafiya a Jigawa,” in ji shi.
Gwamna Namadi ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da saka hannun jari a gine-ginen asibitoci, bunƙasa ma’aikatan lafiya da aiwatar da sauye-sauye domin samar da ingantaccen kiwon lafiya ga al’ummar jihar baki ɗaya.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Email Telegram WhatsApp

Related Posts

ANKARAWA SARAKUNAN GARGAJIYA ALBASHI DA KIMANIN KASHI 300

KUNGIYAR YAN JARIDU TA KASA RESHEN JIHAR JIGAWA TA RABA KUDADE GA YAYAN KUNGIYAR DOMIN GUDANAR DA SHAGULGULAN SALLAH BABBA

TSOHON DAN MAJALISAR WAKILAI NA TARAYYA YA KOMA JAM, IYYAR NDC, WAJEN SANATA KWANKWASO

KANO STATE SSG, DG NPC BAFFA DAN’AGUNDI , COMMISSIONERS , SPECIAL l ADVISERS TO PLAN 3-YEAR ANNIVERSARY y OF f GOV . ABBA KABIR YUSUF f

KUNGIYAR YAN JARIDU TA KASA RESHEN JIHAR JIGAWA TA TSIGE SHUGABAN YAN JARIDU MASU DAUKARWA, GIDAJEN JARIDU NA WAJE LABARAI

JIGAWA STATE COUNCIL REMOVES CORRESPONDENTS’ CHAPEL CHAIRMAN DUE TO EXIT FROM JOURNALISM AND PARTISAN POLITICAL CANDIDACY

Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

ANKARAWA SARAKUNAN GARGAJIYA ALBASHI DA KIMANIN KASHI 300

May 26, 2026

KUNGIYAR YAN JARIDU TA KASA RESHEN JIHAR JIGAWA TA RABA KUDADE GA YAYAN KUNGIYAR DOMIN GUDANAR DA SHAGULGULAN SALLAH BABBA

May 26, 2026

GWAMNATIN JIHAR JIGAWA TARE DA HADIN GWIWAR AFRICAN PERINATAL SOCIETY ZASU INGANTA HARKOKIN LAFIYA TUN DAGA TUSHE

May 25, 2026
Advertisement
© 2026 MURYAR AREWA A YAU. Developed ny: ENGRMKS & CO.
  • Home
  • About Us
  • Disclaimer
  • Get In Touch
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.