Manyan jiga-jigai a gidan siyasar Gawuna na shirin komawa jam’iyyar APC a Kano
Wata tawagar ’yan siyasa masu biyayya ga tsohon Mataimakin Gwamnan Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, ta kai ziyarar goyon baya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf da Mataimakinsa, Murtala Sule Garo, gabanin shirin sauya sheƙarsu daga Jam’iyyar NDC zuw APC.
Mai magana da yawun Gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

Tawagar, wadda wani na hannun daman Gawuna, Hon. Muhammad Badaru Umar, ya jagoranta, ta ƙunshi Mataimakin Shugaban NDC na Jihar Kano, Hon. Ali Datti Yako; Hon. Mansur Isa Gawuna; Hon. Uba Tanko Mijinyawa, wanda aka fi sani da Uba Danzainab; da sauran manyan ’yan siyasa.
Sauran sun haɗa da Hon. Aminu Umar Faruk, Hon. Sani Jibrin, Hon. Salisu Muhammad, Hon. Musa Sani Indabo, Hon. Muhammad Kabir Bala, Hon. Hassan Abba Abdullahi da Comrade Abdurrahman Muhammad.
Da yake magana yayin ziyarar, Muhammad Badaru Umar ya ce sun yanke shawarar ganawa da Gwamna Yusuf ne saboda kishinsu da ci gaban Jihar Kano.
Ya bayyana cewa ziyarar wani ɓangare ne na shawarwarin da suke gudanarwa da kuma ƙoƙarin bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar.
Shi ma Ali Datti Yako ya ce al’ummar Kano sun san irin ƙoƙarin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ke yi wajen sauya fasalin jihar.
“Duk duniya ta san cewa Gwamna Yusuf yana aiki tuƙuru domin sauya fasalin Jihar Kano,” in ji shi.
Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da ake samun sauye-sauyen siyasa a Kano gabanin zaɓen 2027, yayin da manyan ’yan siyasa ke sake duba alaƙarsu da jam’iyyun siyasa.
