Gwamna Namadi: Tallafin Irin Shuka na Gwamnatin Tarayya Zai Taimaka wa Manoman Jigawa Su Farfado daga Asarar Rashin Isasshen Ruwan Sama
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya bayyana jin daɗinsa kan tallafin da Gwamnatin Tarayya ta samar domin taimaka wa manoman da suka yi asarar amfanin gona sakamakon ƙarancin ruwan sama da rashin daidaiton damina.
Gwamnan ya ce rabon ingantattun irin shuka da aka tantance zai taimaka wa manoman da abin ya shafa wajen sake shuka, dawo da wani ɓangare na amfanin gonarsu da suka rasa, tare da ƙarfafa samar da isasshen abinci da ingantaccen abinci mai gina jiki a jihar.
Gwamnan ya bayyana hakan ne cikin wani jawabin da Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa, Engr. Aminu Usman, ya gabatar a madadinsa, a wajen ƙaddamar da shirin “Seeds for Renewed Hope Programme” a Dutse ranar Alhamis.
Shirin, wanda National Agricultural Seeds Council (NASC) ke aiwatarwa tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Jigawa, zai samar da ingantattun irin wake, ridi da gyada ga kusan manoma 5,000 a jihar, domin ba su damar farfaɗo da noman da suka rasa a cikin sauran lokacin daminar.
Gwamna Namadi ya yaba wa Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, bisa wannan mataki da ya ce ya zo a daidai lokacin da manoma da dama ke fuskantar matsalolin asarar amfanin gona sakamakon ƙarancin ruwan sama.
Ya ce tallafin zai bai wa manoman da abin ya shafa damar sake shuka, farfaɗo da noma da kuma ƙara juriya wajen fuskantar irin waɗannan matsaloli a nan gaba.
Gwamnan ya kuma yabawa NASC bisa yadda take gudanar da ayyukanta na haɓaka, tsara dokoki, tabbatar da inganci da kuma tantance irin shukar da ake amfani da su a Najeriya.
A cewarsa, wannan na ƙara wa manoma kwarin gwiwar cewa irin shukar da aka raba musu ya cika ƙa’idojin da ake buƙata.
Noma shi ne ginshiƙin tattalin arzikin Jigawa
Gwamna Namadi ya ce wannan tallafi na da matuƙar muhimmanci ga Jigawa, saboda noma shi ne babban ginshiƙin tattalin arzikin jihar kuma shi ne tushen rayuwar mafi yawan al’ummar jihar.
Ya bayyana cewa idan aka samu matsalar ruwan sama, illar hakan ba ta tsaya a gonaki kawai ba, domin tana shafar kuɗin shiga na iyalai, samar da abinci, ayyukan yi a karkara, kasuwanci da walwalar jama’a.
Gwamnan ya kuma jajanta wa manoman da suka yi asara a wannan kakar, tare da tabbatar musu cewa Gwamnatin Jihar Jigawa ta fahimci irin ƙalubalen da suke fuskanta.
A ƙarƙashin shirin, za a raba tan 32 na irin wake, wanda aka shirya cikin buhuna 3,200, kowanne mai nauyin kilogram 10, ga manoma 3,200.
Haka kuma, za a raba tan 8.35 na irin ridi, cikin buhuna 935 masu nauyin kilogram 10, ga manoma 835.
Sannan za a samar da irin gyada, wanda aka shirya cikin buhuna masu nauyin kilogram 10, ga manoma 900.
Gwamna Namadi ya buƙaci waɗanda suka amfana da tallafin da su yi amfani da irin shukar yadda ya kamata, tare da bin shawarwarin jami’an kula da harkokin noma kan yadda za a shirya gona, lokacin shuka, tazarar shuka, yaƙi da kwari da kuma kula da amfanin gona bayan shuka.
Ya ce Gwamnatin Jihar Jigawa za ta ci gaba da ƙarfafa ayyukan jami’an wayar da kan manoma, domin tabbatar da cewa ba wai an ba manoma kayan noma kawai ba, har ma an ba su ilimin da zai taimaka musu wajen samun amfanin gona mai yawa.
Tallafin ya dace da ajandar maki 12 ta gwamnatin Jigawa
Gwamna Namadi ya ce wannan tallafi ya yi daidai da Ajandar Maki 12 ta gwamnatinsa da kuma shirinta na sauya fasalin harkar noma a jihar.
Ya ce manufofin sun haɗa da samar da ingantaccen noma mai ɗorewa, ƙara samar da abinci, samar da ayyukan yi, tallafa wa manoma, faɗaɗa ban ruwa da aikin injina, ƙara darajar amfanin gona da kuma jawo hannun jarin masu zaman kansu.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Jihar Jigawa ta sanya odar takin gargajiya (organic fertiliser) a matsayin wani zaɓi na daban ga takin zamani na sinadarai.
Ya tabbatar wa Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci ta Tarayya da NASC cewa gwamnatin jihar za ta ba da cikakken haɗin kai domin tabbatar da cewa tallafin ya isa hannun manoma na gaskiya kuma ya cimma manufar da aka sanya masa.
Kyari: Tinubu ya umarci a kai tallafin cikin lokacin damina
Da yake jawabi a wajen taron, Ministan Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari, CON, ya ce Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da tallafin ne domin taimaka wa manoma su farfaɗo da wani ɓangare na lokacin noma da suka rasa sakamakon ƙarancin ruwan sama.
Ministan ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne ya amince da shirin tare da bayar da umarnin cewa a tabbatar da isar da tallafin ga manoman da abin ya shafa cikin sauran lokacin daminar.
Ya bayyana cewa kowace jiha da za ta amfana da shirin za ta samu tan 32 na ingantaccen irin wake, tan 9 na ingantaccen irin gyada da kuma tan 8.35 na ingantaccen irin ridi.
A Jigawa, ana sa ran shirin zai amfani kusan gidajen manoma ƙanana 4,935.
Kyari ya ce an zaɓi wake, gyada da ridi ne saboda amfanin gonakin suna da gajeren lokacin girma, kuma ingantattun nau’insu na iya kai wa lokacin girbi cikin sauran lokacin daminar.
Ministan ya kuma yabawa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa ci gaba da saka hannun jari wajen ban ruwa, aikin injinan noma, ayyukan wayar da kan manoma da samar da ingantattun kayan noma, tare da haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki.

NASC ta tabbatar da ingancin irin da ake rabawa
A nasa jawabin, Darakta-Janar na National Agricultural Seeds Council, Fatuhu Mohammed, ya ce majalisar za ta ci gaba da tabbatar da cewa manoma sun samu ingantattun kayan shuka.
Ya ce hakan na gudana ne ta hanyar tantance irin shuka, tabbatar da inganci, rajistar nau’ikan iri, gwaje-gwajen dakunan bincike da kuma sanya ido kan bin ƙa’idojin masana’antar irin shuka.
Ya kuma yabawa Gwamna Namadi kan zuba jari da gwamnatinsa ke yi a fannin ban ruwa, aikin injina, ingantattun kayan noma da ayyukan wayar da kan manoma, da kuma manufofin da ke ƙarfafa masu zaman kansu su zuba jari a harkar noma.
An gudanar da bikin ƙaddamar da shirin ne tare da halartar Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci ta Tarayya, NASC, Gwamnatin Jihar Jigawa, ƙungiyoyin manoma da sauran masu ruwa da tsaki, domin tabbatar da cewa ingantattun irin shukar sun isa hannun manoma cikin gaggawa kafin ƙarshen lokacin daminar.
