JIGAWA SHEKARA 35: GWAMNA NAMADI YA SAKE JADDADA ANIYAR KARE ZAMAN LAFIYA, ADALCI DA CI GABA MAI ƊOREWA
Yayin da Jihar Jigawa ke cika shekaru 35 da kafuwarta,
Gwamna Malam Umar Namadi ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, ƙarfafa adalci da kuma faɗaɗa damar samun ci gaba mai ɗorewa ga al’ummar jihar.
Gwamnan ya kuma yaba da girmama irin gudunmawar da iyayen da suka kafa jihar, shugabannin da suka gabata da kuma al’ummar Jigawa suka bayar wajen gina tare da ciyar da jihar gaba.
An kafa Jihar Jigawa ne a ranar 27 ga watan Agustan 1991, a ƙarƙashin gwamnatin mulkin soja ta tarayya karkashin jagorancin Janar Ibrahim Badamasi Babangida, GCFR. Kafuwar jihar na daga cikin matakan sake fasalin tarayyar Najeriya domin kusantar da gwamnati ga jama’a tare da samar da ci gaba cikin daidaito.
An ƙirƙiri Jihar Jigawa ne daga tsohuwar Jihar Kano, inda aka sanya Dutse a matsayin babban birninta. Tun daga wannan lokaci, jihar ta ci gaba da samun bunƙasa sakamakon gudunmawar gwamnatoci daban-daban, hukumomi da kuma tsararrakin al’ummarta.
A cikin sakonsa na tunawa da cikar shekaru 35 da kafuwar jihar, Gwamna Namadi ya bayyana wannan lokaci a matsayin na godiya ta musamman ga Allah Maɗaukakin Sarki, yin nazari kan abubuwan da suka gabata da kuma sabunta ƙuduri.
Ya ce bikin cikar shekaru 35 wata dama ce ta yaba wa jaruman kishin ƙasa da suka bayar da hangen nesa, fafutuka, sadaukarwa da hidimar jama’a waɗanda suka taimaka wajen kafa Jihar Jigawa tare da ci gaba da gina ta.
Gwamna Namadi ya karrama iyayen da suka assasa jihar, dattawan ƙasa, shugabannin addini da na al’umma, ma’aikatan gwamnati, ƙwararru, mata da matasa, ƙungiyoyin farar hula, abokan hulɗar ci gaba da kuma daukacin al’ummar jihar saboda irin gudunmawar da suka bayar.
Gwamnan ya kuma amince da irin hidimar da shugabannin jihar daban-daban, masu rai da waɗanda suka rasu, suka bayar. Cikin waɗanda ya ambata akwai:
Manajin farko na mulkin soja, Manjo Janar Olayinka Sule;
Zaɓaɓɓen Gwamnan farar hula na farko, Alhaji Ali Sa’ad Birnin-Kudu;
Birgediya Janar Ibrahim Aliyu;
Kanal Rasheed Alade Shekoni;
Laftanar Kanal Abubakar Zakariya Maimalari;
Alhaji Ibrahim Saminu Turaki;
Alhaji Sule Lamido; da
Alhaji Muhammad Badaru Abubakar.
Haka kuma, Gwamna Namadi ya yaba da gudunmawar tsoffin mataimakan gwamnoni, ’yan majalisa, alkalai, kwamishinoni, shugabannin ma’aikatan gwamnati, sakatarorin dindindin, shugabannin ƙananan hukumomi da sauran ma’aikatan gwamnati da suka yi wa jihar hidima ta fannoni daban-daban.
Gwamnan ya kuma jinjinawa masarautun Hadejia, Kazaure, Gumel, Ringim da Dutse, tare da hakimai, dagatai da masu unguwanni, malamai da shugabannin al’umma saboda rawar da suke ci gaba da takawa wajen kare al’adun jihar, tabbatar da zaman lafiya da kuma zama gada tsakanin gwamnati da jama’a.
Gwamna Namadi ya ce ci gaban da Jihar Jigawa ta samu tsawon shekaru 35 ya samo asali ne daga haɗin gwiwa da ƙoƙarin al’ummarta.
Ya amince da gudunmawar manoma, ’yan kasuwa, malamai, ma’aikatan lafiya, masu sana’o’in hannu, masana, ’yan kasuwa masu zaman kansu, jami’an tsaro, shugabannin addini, ma’aikatan gwamnati da sauran al’umma.
“Tun daga farkon gina hukumomin jihar har zuwa yau, Jigawa ta samu ci gaba ne sakamakon jajircewa da aikin al’ummarta,” in ji Gwamnan.
Gwamna Namadi ya bayyana cewa babbar hanyar girmama iyayen da suka kafa jihar da shugabannin da suka gabata ba wai kawai tuna sunayensu ba ne, sai dai ci gaba da riƙe manufofi da kyawawan dabi’un shugabancinsu.
A cewarsa, waɗannan manufofi suna buƙatar ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, adalci, samar da dama ga jama’a da kuma gudanar da dukiyar jama’a cikin gaskiya da riƙon amana.
Ya kuma jaddada muhimmancin bai wa masu rauni kulawa, girmama dattawa, zuba jari wajen bunƙasa matasa da kuma ƙarfafa hukumomin da za su dore fiye da kowane zamani ko gwamnatin mutum ɗaya.
Gwamnan ya bayyana bikin tunawa da cikar shekaru 35 a matsayin lokacin “girmama jiya, yi wa yau hidima tare da shirin gobe.”
Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su sabunta ƙudurinsu na gina Jigawa mai zaman lafiya, wadata, haɗa kowa da kowa, ladabi da kuma dogaro da ilimi.
Gwamna Namadi ya roƙi al’ummar Jihar Jigawa da su ci gaba da nuna fahimta, haƙuri da goyon baya ga gwamnatinsa yayin da take aiwatar da manufofinta na ci gaba, waɗanda suka ta’allaka kan ci gaba mai ɗorewa, walwalar tattalin arziki da zamantakewa, zaman lafiya da wadata ga kowa.
A ƙarshe, Gwamna Namadi ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya saka wa duk waɗanda suka yi wa jihar hidima da alheri, Ya gafarta wa waɗanda suka rasu, Ya ƙara wa masu rai ƙarfi da lafiya, tare da ci gaba da albarkaci Jihar Jigawa da Tarayyar Najeriya baki ɗaya.
