JIGAWA DA RANO AIR SUN RATTABA HANNU KAN YARJEJENIYAR ZIRGA-ZIRGAR JIRAGEN ABUJA–DUTSE
: Gwamnatin Jihar Jigawa ta rattaba hannu kan yarjejeniyar haɗin gwiwa da kamfanin Rano Air Limited, domin fara zirga-zirgar jiragen sama na kasuwanci tsakanin Abuja da Dutse, babban birnin jihar.
An rattaba hannu kan yarjejeniyar ne a gidan gwamnatin jihar da ke Dutse, a wani biki da Mataimakin Gwamnan Jigawa, Injiniya Aminu Usman, ya jagoranta, wanda ya wakilci Gwamna Malam Umar Namadi.
A ƙarƙashin yarjejeniyar, kamfanin Rano Air zai gudanar da zirga-zirgar jiragen sama tsakanin Abuja–Dutse–Abuja sau uku a mako, wato ranakun Litinin, Laraba da Juma’a, ta amfani da jirgin da zai iya ɗaukar fasinjoji 50.
A nasa ɓangaren, gwamnatin jihar za ta taimaka wajen bunƙasa wannan hanyar zirga-zirga a farkon matakanta, tare da samar da yanayin da zai ba da damar ci gaba da gudanar da harkokin jiragen cikin nasara.
B Da yake jawabi a wajen bikin, Mataimakin Gwamnan ya bayyana yarjejeniyar a matsayin wani muhimmin mataki na ƙoƙarin gwamnatin jihar na ƙarfafa harkokin sufuri da kuma inganta hanyoyin sadarwa da zirga-zirga ga al’ummar Jigawa.
Ya ce fara zirga-zirgar jiragen kasuwanci kai tsaye tsakanin Dutse da Abuja zai samar da wata sabuwar hanyar sufuri, tare da buɗe ƙofofin sabbin damammakin tattalin arziki ga jihar.
Ya ce: “Fara zirga-zirgar jiragen kasuwanci tsakanin Dutse da Abuja ba wai kawai ƙara wata hanyar jirgin sama ba ce. Hakan na nufin buɗe sabon babi na damammakin tattalin arziki ga jiharmu.”
Mataimakin Gwamnan ya ƙara da cewa Jigawa na fuskantar ƙaruwa a harkokin noma, kasuwanci, zuba jari, ilimi, yawon buɗe ido da kuma gudanar da ayyukan gwamnati, lamarin da ya sa ake ƙara buƙatar ingantaccen, abin dogaro da kuma sauƙaƙa tsarin sufuri.
Ya ce samar da zirga-zirgar jiragen sama akai-akai zai sauƙaƙa wa masu zuba jari, ‘yan kasuwa, jami’an gwamnati, abokan hulɗar ci gaba, ƙwararru da kuma baƙi shiga da fita daga Jihar Jigawa.
Ya kuma bayyana cewa hakan zai taimaka wajen mayar da Jigawa wata jiha mai jan hankalin masu zuba jari da harkokin kasuwanci.
Mataimakin Gwamnan ya jaddada cewa haɗin gwiwar za a gudanar da shi ne bisa ɗaukar nauyi, gaskiya da rikon amana, da kuma auna sakamako, inda gwamnatin jihar ke sa ran kamfanin jirgin zai kiyaye ƙa’idojin tsaro, amincin aiki, ƙwarewa da kuma kyakkyawar mu’amala da fasinjoji.
Ya ce: “Muna sa ran Rano Air zai kiyaye manyan ƙa’idojin tsaro, amincin aiki, ƙwarewa da kuma kyakkyawar hidima ga abokan ciniki. Haka kuma muna sa ran za a bi yarjejeniyar, jadawalin zirga-zirgar jirage da kuma ci gaba da tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu.”
Rano Air ya tabbatar da jajircewa
Da yake nasa jawabin, Manajan Daraktan Rano Air Limited, Alhaji Lawan Sabo Bakin Zuwo, ya ce kamfanin zai fara gudanar da zirga-zirgar jiragen kasuwanci tsakanin Abuja da Dutse, wanda zai ƙara samar da wata hanyar sufuri ga al’ummar jihar.
Ya ce: “Mun fahimci muhimmancin wannan hidima. Muna tabbatar wa gwamnatin Jihar Jigawa da al’ummar jihar cewa Rano Air ya himmatu sosai wajen ganin wannan haɗin gwiwa ya yi nasara.”
Alhaji Lawan Sabo Bakin Zuwo ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa jagoranci da goyon bayan da yake bayarwa, yana mai cewa jajircewar gwamnan wajen ci gaban Jigawa ta taka muhimmiyar rawa wajen ganin an samu wannan yarjejeniya.
Ya ce: “Muna matuƙar godiya ga jagoranci mai hangen nesa da goyon bayan Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, wanda jajircewarsa wajen ci gaban jihar ya taimaka matuƙa wajen ganin wannan haɗin gwiwa ya samu.”
Ya kuma nuna godiya ga Mataimakin Gwamnan da gwamnatin Jihar Jigawa bisa haɗin kai da amincewar da suka nuna wa Rano Air.
Manajan Daraktan ya ce tsaro zai kasance babban abin da Rano Air zai fi bai wa muhimmanci, tare da tabbatar da ingantaccen aiki, amincin zirga-zirga da kyakkyawar hidima ga fasinjoji.
Ya ce: “A Rano Air, tsaro shi ne babban abin da muke bai wa fifiko. Mun himmatu wajen kiyaye mafi girman ƙa’idojin tsaro, amincin aiki, ingantaccen gudanar da zirga-zirga da kuma kyakkyawar hidima ga abokan ciniki.”
Ya bayyana cewa wannan haɗin gwiwa ba zai tsaya ga harkokin sufuri kaɗai ba, domin zai taimaka wajen haɗa iyalai, bunƙasa kasuwanci da zuba jari, sauƙaƙa ayyukan gwamnati da kuma bayar da gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikin Jihar Jigawa.
Ya ce: “Mun yi imanin cewa wannan haɗin gwiwa zai haɗa iyalai, ya sauƙaƙa harkokin kasuwanci da zuba jari, ya tallafa wa ayyukan gwamnati, tare da bayar da gagarumar gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikin Jihar Jigawa.”
Related Posts
Add A Comment
