Close Menu
  • Home
  • Kasuwanci
  • Nishadi
  • Features
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Karin Wasu
    • Noma da Kiwo
    • Sauyin Yanayi
    • Fasaha
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) Instagram
MURYAR AREWA A YAU
Subscribe
  • Home
  • Kasuwanci

    GWAMNAN JIHAR KANO ALH ABBA KABIR YUSUF YA SAUKE KWAMISHINAN ZUBA JARI DA KASUWANCI, DAGA KAN MUKAMINSA

    March 26, 2026

    FILIN JIRGIN SAMAN DUTSE JIHAR JIGAWA ZAI DINGA KARBAR KAYA NA KAGO

    February 23, 2026

    Zulum Leads Fintiri, Buni to Meet New World Bank Director

    November 14, 2025

    Gwamnatin Najeriya ta roki jama’a su rage cin ganda (ponmo) kada kamfanin sarrafa fata na kasar ya durkushe

    November 14, 2025

    STANDARD ORGANIZATION OF NIGERIA AND FEDERAL MINISTRY OF TRADE ARE GOING TO WORK TOGETHER

    November 8, 2025
  • Nishadi

    WANI : MAGIDANCI MAI MATA BIYU A BAUCHI, YA KASHE DAN ACABA DON SAMUN KUDIN KARA AUREN MATA TA UKU

    October 22, 2025

    Qausain TV appoints Adam A. Zango as Director-General

    October 8, 2024

    Young Jonn Sets To Thrill Fans With Electrifying Performance In Abuja

    September 29, 2024

    Why Bobrisky was separated from other inmates – Prison experts

    September 27, 2024
  • Features

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA ZATA BULLO DA SABBIN DABARUN WARWARE MATSALOLIN MANOMA DA MAKIYAYA,TARE DA TANTANCE KAN IYAKOKI

    April 14, 2026

    AN SHAWARCI MALAMAI DAKE GUDANAR DA DA, AWAH DA SU DINGA KARANTAR DA WADANDA AKA MUSULUNTAR DOMIN SU SAN ADDININ MUSULUNCI, INJI BARR, YAHYA IBRAHIM ALIYU R

    April 14, 2026

    GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI DAN MODI YA CE, ILIMI BABBAN JARI DOMIN CIGABAN JIHAR JIGAWA,DAMA KASA BAKI DAYA

    April 12, 2026

    JIGAWA STATE IS A WRONG PLACE TO COMMIT CRIME AS AFFIRMED BY THE DECISIONS OF THE SUPREME COURT OF NIGERIA.

    April 11, 2026

    YAN FASHIN DAJI NA FAMA DA ANNOBAR AMAI DA GUDAWA, HAR TA YI AWON GABA DA WASU DAGA CIKIN SU ZUWA LAHIRA

    April 9, 2026
  • Labarai

    JIGAWA A ROLE MODEL FOR HEALTH SECTOR REFORMS IN NIGERIA – ZAMFARA PS PUBLIC SERVICE OFFICE

    April 1, 2026

    AN TSARE WANI DIREBAN MOTAR MATAR SARKI BISA ZARGIN SATAR GWALA – GWALAI NA MILIYOYIN KUDI MASU TSADAR GASKE

    April 1, 2026

    CELEBRATING A VISIONARY LEADER r AT 74TH : DG DAN’AGUNDI FELICITATES PRESIDENT TINUBU ON HIS BIRTHDAY

    March 29, 2026

    KUNGIYAR TALLAFAWA MARAYU DA GAJIYAYYU TA YAHAYA IBRAHIM ALIYU CHARITY FOUNDATION TA MIKA SAKON TA, AZIYYA

    March 29, 2026

    EMIR BAYERO RALLIES NIGERIANS IN POWERFUL PRAYERS PRAYERS FOR FOR r PEACE , SECURITY AND ECONOMIC REVIVAL.

    March 23, 2026
  • Siyasa

    REJOINDER: THE FALLACY OF THE “COMMANDER AND THE BURDEN OF INTEGRITY

    April 5, 2026

    MATASAN JIHAR KANO SUNCE :-MURTALA SULE GARO NE YAFI CANCANTAR ZAMA MATAIMAKIN GWAMNAN JIHAR KANO

    April 4, 2026

    HON ALHASSAN ADO DOGUWA, YACE WAJIBI NE AYI KYAKYKYAWAN SHIRI DOMIN TUNKARAR ZABEN SHEKARA TA 2027 DOMIN KUWA AKWAI GAGARUMAR MATSALA

    April 2, 2026

    GANDUJE PUSHES GARO FOR KANO DEPUTY GOVERNOR AS APC STAKEHOLDERS KICK AGAINST MOVE

    April 1, 2026

    AN BUKACI MAGOYA BAYAN SHEIKH IBRAHIM KHALIL DASU FITO RANAR ALHAMIS DOMIN TARBARSA, A FILIN JIRGIN SAMAN MALAM AMINU KANO

    April 1, 2026
  • Tsaro

    JIGAWA STATE IS A WRONG PLACE TO COMMIT CRIME AS AFFIRMED BY THE DECISIONS OF THE SUPREME COURT OF NIGERIA.

    April 11, 2026

    YAN FASHIN DAJI NA FAMA DA ANNOBAR AMAI DA GUDAWA, HAR TA YI AWON GABA DA WASU DAGA CIKIN SU ZUWA LAHIRA

    April 9, 2026

    KHADIJA ISAH THE 9 YEAR OLD VICTIM OF BRUTAL RAPE GOT JUSTICE .

    April 9, 2026

    GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI DAN MODI YA YI WA WASU MASU ZAMAN GIDAN GYARAN HALI AFUWA 12

    March 19, 2026

    GWAMNATIN JIHAR KANO TA DAUKI MATAKIN TSAURARA TSARO YAYIN SALLAR IDI DA ZA, A GABATAR NAN GABA KADAN DOMIN BIN DOKA DA ODA

    March 18, 2026
  • Wasanni

    Ndume Unity Cup 2025: Drama, Determination, and Dominance as Matchday 1 Unfolds.

    November 15, 2025

    MAGOYA BAYAN KUNGIYAR KWALLON KAFA TA KATSINA UNITED TA SUN RAUNATA YAN WASAN KUNGIYAR KWALLON KAFA TA BARAU FC TARE DA YIWA MOTOCIN BARAU FC ROTSE

    November 8, 2025

    NASARAR GIWA UNITED FILIN SUKUWA

    October 24, 2025

    new Kano-based football club, Bichi First FC, has appointed renowned journalist Muzammil Dalha Yola as its Media Officer.

    September 12, 2025

    Kungiyoyin Kwallon Kafa Na Barau da Kano pillars Duk Na Y’aya”n Jihar kano ne Ba Na Mutum Daya bane – :Inji Adamu Abdullahi karkasara

    August 19, 2025
  • Karin Wasu
    1. Noma da Kiwo
    2. Sauyin Yanayi
    3. Fasaha
    4. View All

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA ZATA BULLO DA SABBIN DABARUN WARWARE MATSALOLIN MANOMA DA MAKIYAYA,TARE DA TANTANCE KAN IYAKOKI

    April 14, 2026

    GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI YA YI ALKAWARIN CI GABA DA TAIMAKA WA MANOMA DA BUNKASA TATTALIN ARZIKI

    March 22, 2026

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA TA KADDAMAR DA KASHI NA UKU NA TALLAFAWA MA, AIKATAN GWAMNATI TA FUSKAR NOMA

    March 13, 2026

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA ZATA HADA GWIWA DA NDDB NA KASAR INDIA DOMIN SAMAR DA MADARA DA BUNKASA KIWON SHANU

    March 10, 2026

    MALIKAWA GARU :- PLANT A TREE TODAY TO FIGHT DESERTIFICATION

    October 16, 2025

    Zulum commissions housing complex for teachers in Mafa

    October 7, 2025

    NiMet Predicts Three-day Thunderstorm, Downpour Nationwide

    October 14, 2024

    NiMET Predicts Three-Day Thunderstorms From Monday

    October 1, 2024

    Zulum: Borno begins export of plastic materials

    October 30, 2025

    Zamkah Technologies Has Signed MOU With Institute For Peace and Conflict Resolution (IPCR)

    September 9, 2025

    Digital Age: How Technology Impacts Modern Marriage

    September 29, 2024

    Artificial Intelligence will replace unskilled workers – Daily Trust

    September 27, 2024

    GWAMNATIN JIHAR JIGAWA ZATA BULLO DA SABBIN DABARUN WARWARE MATSALOLIN MANOMA DA MAKIYAYA,TARE DA TANTANCE KAN IYAKOKI

    April 14, 2026

    AN SHAWARCI MALAMAI DAKE GUDANAR DA DA, AWAH DA SU DINGA KARANTAR DA WADANDA AKA MUSULUNTAR DOMIN SU SAN ADDININ MUSULUNCI, INJI BARR, YAHYA IBRAHIM ALIYU R

    April 14, 2026

    GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI DAN MODI YA CE, ILIMI BABBAN JARI DOMIN CIGABAN JIHAR JIGAWA,DAMA KASA BAKI DAYA

    April 12, 2026

    JIGAWA STATE IS A WRONG PLACE TO COMMIT CRIME AS AFFIRMED BY THE DECISIONS OF THE SUPREME COURT OF NIGERIA.

    April 11, 2026
MURYAR AREWA A YAU
Home » A NIJERIYA :-YAU CE RANAR TUNAWA DA SIR, AHMADU BELLO SARDAUNA DA SIR ABUBAKAR TABAWA BALEWA

A NIJERIYA :-YAU CE RANAR TUNAWA DA SIR, AHMADU BELLO SARDAUNA DA SIR ABUBAKAR TABAWA BALEWA

By Ali MuhammadJanuary 15, 2026 Uncategorized 7 Mins Read
Screenshot 20260115 083509
Share
Facebook Twitter Email Telegram WhatsApp

 

Yau rana ce mai cike da tarihi a Najeriya!

A rana irin ta yau a 1966 ne aka kashe Firaiministan Najeriya na farko, Tafawa Ɓalewa da Firimiyan Arewa, Ahmadu Bello da wasu jiga-jigan ƴansiyasa da sojoji a yunƙurin sojoji na juyin mulki.

Ahmadu Bello ne firimiyan jihar Arewa na farko a tarihi kuma akwai wasu sanannun mutane da suka riƙe muƙamin minista a ƙarƙashinsa.

Wane Irin Kisa Akayiwa Sir Ahmadu Bello Sardauna? Yau Shekaru 60 Kenan!!

Kisan da akaima Sardauna a gidan Gwamnatin Jahar Arewa dake Kaduna. Da yawan mutane sunyi maganganu, wasu maganganunma ba su da kangado, babu ilimi ko daya a ciki. Dayawan labaran da mutane suke yadawa hankali bazai dauka ba.

Hakan yasa na zurfafa bincike sosai dan mu gane shin wane irin kisa akayiwa Sardauna? Wasu mawakan hausa da wasu mutane makusantar Sardauna, sun bada wasu labarai wayanda hankali ba zai dauke su ba.

Bincike ya tabbatar da cewa shi wanda ya jagoranci, kisan su Sardauna Manjo Patrick Chukuma Kaduna Nzeogwu, ya dade da kullantar Sardaunan a ransa, hakan ya sa ya fara horar da wasu sojoji wanda mafi yawancinsu yan Arewa ne.

NZEOGWU YA KADDAMAR DA SAMAME MASU SUNA KAMAR HAKA. OPERATION.

Ya kaddamar da Samame masu Sunaye Kamar Haka

Damisa
Zaki
Giwa

Irin wannan samamen shi Nzeogwu ya yi ta ba wa sojojin horo a kai. Sukan kansu sojonin basu san dalilin da yasa yake basu wannan horon ba. Kullun dare yakan tarasu suyi tayin wannan Atisayen har Asuba. Duk da cewa manyan sojoji na kallonsa sukansu basu da masaniyar dalilin da yasa yake basu wannan horon ba, ya fake da cewar ya kamata ace sojoji na cikin shiri, kuma su rika jiran ko ta kwana.

Ranar 15 ga watan Janairun 1966, juma’a wurin karfe goma Sha biyu na dare, Nzeogwu ya kwaso wasu kuratan sojoji su 45, wasu ma sukace su 50, yan Arewacin Najeriya. Nzeogwu, ya kai su wani wuri inda a yanzu wata makarantar aikin noma take a Mando. A wancan lokacin wurin kungurmin dajine. Daga nan ne suka taso suka nufo Gidan Sardauna. Bincike ya tabbatar da cewar ya kashe wani soja daya da ya nemi yai masa taurin Kai. Kamar yadda abun ya faru wannan sojan ya tsananta da tambayar cewa wane irin aiki na musamnan za suyi? A inane kuma za suyi wannan aikin na musamman? Kuma yaya yanayin aikin yake?

Bayan isowarsu kofar gidan Sardauna, Nzeogwu, ya nunawa wayannan sojojin daya kwaso cewar kunsan ko nan gidan waye? Suka amsa masa da cewar gidan baban duk wani dan Arewa ne Sardauna. Nzeogwu yace musu to mai Gidannan shi muka fito kashewa. Nan take wani Sagent Bayaraben Ilori, Sagen Duru, yace Allah ya kiyaye shi, ya sa hannu a kashe Babansa. Bincike ya tabbatar da cewa Sagen Duru yayi yunkurin tsalake titi ya gudu, amma nan take Nzeogwu, ya harbeshi.

Makaman da Nzeogwu yazo dasu gidan Sardauna sun fi karfin na juyin mulki sai dai na yaki da wata kasa. Nan take Nzeogwu ya umarci wani kurtun soja dan asalin Jahar Kebbi Musa Manga, yace ya harba bindigar da ake amfani da ita wurin kakkabo jirgin saman yaki MM 400× a saman rufin nakin da Sardauna yake.

Karar wannan bindigar ta tada hankalin duk wani mutumin dake Unguwar shanu, da Unguwar sarki. Wannan bindigar itace tasa rufin dakin ya Kamada wuta. Sardauna da matansa da yaran da yake rike da su na yan’,uwa da abokan arziki da duk ma’aikatan dake gidan sun taru a farfadiyar da ake wajen fakin din mota na gidan.

Sardauna ya tsinci kan sa a wani hali na ba shi da wani mataimaki sai na Allah. Ba shi da makamin da zai kare kansa ballema ya kare iyalansa dashi. Bincike ya tabbatar da cewar anan farfajiyar ajiye motocin ne Nzeogwu ya samu Sardarna da matansa guda uku da Larai matar Ali Odilin Sardauna, da Ali Odilin.

Anan an samu mabambamtan maganannu, matan Sardauna Jabbo da Goggon Bichi sun bada labari iri daya, duk da cewar ba lokaci daya akayi hirar da su ba.

JABBO.

Tace duk kan mu muna cikin fargaba mun rude saboda matsanancin karar harbe harbe da mu ke ji a wannan lokacin. Sardauna na tsaye ne yana jan carbi, Hafsat uwargidansa ta na rungume da shi dukkanmu muna kuka mun rasa inda zamu saka kan mu. Da abubuwa sukayi tsanani shi Sardauna yace mana ni tawa ta ka re ku nake ma addu’ar Allah ya kare ku daga sharin waɗannan mutanan. Hafsat ta rike Sardauna da karfin tsiya nima ina manne da jinkinsa haka Goggon Bichi, Larai matar Ali Odali na kusa dani.

Lokacin da Nzeogwu ya zo, ya zo ne da wata fitila mai haske irinta ta mafarauta a goshinsa da yake gidan akwai duhu babu wuta da farin hankici a wuyansa. Da yake muna da yawa da yara damu matanshi mun kewayashi a wannan lokacin.

Nzeogwu ya yi ta mana barazanar cewa idan bamu kauce ba zai harbemu ya kashe mu dukkan mu. Amma mukayi burus da shi. Bayan kokarin sa mana karfi da yayi mu kayi masa turjiya, yasa kan bindiga ya buge ni a goshi, jini na yai tsartuwa na fadi sumammiya. Tace kamar yadda abubuwa suka faru a nan ne dai Nzeogwu ya harbi Sardauna a goshi da zuciyarsa

GOGGON BICHI.

Tace lokacin da Nzeogwu yazo da fitila mai haske a goshin sa da farin hankici a wuyansa. Mu kuma dukkanmu mun kewaye Sardauna, Hafsat ta rike shi kam-kam. Jabbo ma na rike da shi nima ina manne da shi. Nzegowu yayi barazanar zai harbe mu, amma mu da yara kuka kawai muke muna salati. Goggon Bichi tace tana da yakinin cewa kafimma shi Nzeogwu ya harbi Sardauna Allah ya zare ran Sardaunan. Ta kawo dalilai kwarara guda biyu da yake tabbatar da abun da ta ke fada.

Abu na farko tace babu yadda za a sa kan bindiga a bugi daya daga cikin matansa har ta fadi ta suma, ace Sardaunan bai yi magana, ba tace abu ne wanda ba mai yiwuba.

Goggon Bichi, ta ce Koda mai zai faru da shi kuwa wallahi Sardauna sai ya yi magana, kai sai dai bayan ransa wallahi ba zai taba ganin yana raye a wulakanta matarsa ba. Dalilinta na biyu Kuma Nzeogwu ya harbi Hafsat kafin ya harbi Sardauna, nan ma tace daga nan ne ma na tabbatar da cewa Sardauna ba shi da rai, wallahi yana dai tsaye ne kawai amma Allah ya zare ransa. Tace har Nzeogwu ya harbe shi ba a ji ihunsa ko Kara ko wata magana ba. Hakan ma ya kara tambatar mana da cewa ya rasu.

Jabbo da Goggon Bichi, da Larai Matar Ali Odilin Sardauna wacce itama ganauce sun tabbatar da cewa in ma da wani namiji a sanda abun ya faru to Ali Odili ne.

Matan na Sardauna guda biyu da Larai Matar Ali Odili sun ce duk mazajen dake gidan sun gudu. Sukace duk wani mutum yau daya tara yan Jaridu yace yasan yadda aka kashe Sardauna, ko a gabansa aka kashe Sardauna karya ya keyi.

Marigayi Sheik Abubakar Gumi, shi ne ya yiwa Sardauna wanka ya tabbatar da cewar tabbas akwai harsashi a goshin Sardauna a goshi aka harbeshi.

Bazan iya kawo dukkan hikayoyin a nan ba amma za a iya neman littafi mai suna Jarumar da ba a rubuta ba, Hafsat Ahmadu Bello, wanda Ladi S. Adamu ta rubuta.

 

Share. Facebook Twitter LinkedIn Email Telegram WhatsApp

Related Posts

GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI DAN MODI YA CE, ILIMI BABBAN JARI DOMIN CIGABAN JIHAR JIGAWA,DAMA KASA BAKI DAYA

GWAMNATIN JIHAR JIGAWA TA MIKA GYARAN FADAR SARKIN HADEJIA

KUNGIYAR DAKE YADA ADDININ MUSULUNCI TARE DA TALLAFIN LIKITOCIN ASIBITIN MALAM AMINU KANO, SUN BADA MAGANI GA MAGUZAWA DAKE WANI YANKIN JIHAR KADUNA

YAHUDAWA DA NASARA BAZASU TABA YARDA DA KAI BA HAR SAI KABI HAYARSU DOMIN SU BATAR DA MUSULMIN DUNIYA INJI LIMAMIN MASALLACIN JUMA, A NA ABUBAKAR SADIQ HANYAR DANTSINKE

YAN MAJALISUN WAKILAI 8 DAGA JIHAR KANO SUN SHIGA JAM, IYYAR APC.

BAFFA BABBA DAN AGUNDI HAS CONGRATULATES DIG

Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

GWAMNATIN JIHAR JIGAWA ZATA BULLO DA SABBIN DABARUN WARWARE MATSALOLIN MANOMA DA MAKIYAYA,TARE DA TANTANCE KAN IYAKOKI

April 14, 2026

AN SHAWARCI MALAMAI DAKE GUDANAR DA DA, AWAH DA SU DINGA KARANTAR DA WADANDA AKA MUSULUNTAR DOMIN SU SAN ADDININ MUSULUNCI, INJI BARR, YAHYA IBRAHIM ALIYU R

April 14, 2026

GWAMNAN JIHAR JIGAWA MALAM UMAR NAMADI DAN MODI YA CE, ILIMI BABBAN JARI DOMIN CIGABAN JIHAR JIGAWA,DAMA KASA BAKI DAYA

April 12, 2026
Advertisement
© 2026 MURYAR AREWA A YAU. Developed ny: ENGRMKS & CO.
  • Home
  • About Us
  • Disclaimer
  • Get In Touch
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.