Bikin Tunawa da Jarumtakar Hadejia: Gwamna Namadi Ya Jaddada Bukatar Kare Tarihi da Al’adu
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya halarci bikin tunawa da tarihin juriyar da Masarautar Hadejia ta yi wajen tunkarar mamayar Turawan mulkin mallaka, inda ya bukaci a kara himma wajen adana tarihi da al’adun gargajiya domin amfanin al’umma masu zuwa.
An gudanar da bikin ne a garin Hadejia, tare da halartar Majalisar Masarautar Hadejia karkashin jagorancin Sarkin Hadejia, da sauran sarakuna, manyan baki da al’ummar masarautar. Gwamnan ya bayyana bikin a matsayin wata gada mai muhimmanci da ke hada tarihi da makoma.
Bikin ya kunshi ayyuka daban-daban da suka hada da nishadantarwa da kuma nuna al’adun gargajiya, domin tunawa da tarihin masarautar da kuma tabbatar da cewa an adana shi yadda ya kamata domin al’ummomi masu zuwa.
Daya daga cikin manyan abubuwan da suka dauki hankali shi ne kaddamar da wani littafi mai suna “Hadejia Emirate: A Centenary History of Colonial Resistance and Transformation (1906–2026)”, wanda aka gabatar a dakin taro na Makarantar Jinya. Littafin ya kunshi tarihin sama da shekaru 100 na jajircewa, shugabanci da sauye-sauye da masarautar ta fuskanta.
Hakazalika, gwamnan ya halarci kaddamar da sabon gidan tarihi na Hadejia (Museum), wanda aka tanada domin ajiye kayayyakin tarihi, bayanai da labarai da ke bayyana dimbin al’adun al’ummar yankin.
Bikin ya kuma hada da faretin durbar a fadar sarki, wanda ya nuna kyawawan al’adun masarautar tare da tabbatar da dorewar al’adu daga zamani zuwa zamani.
A jawabin da ya gabatar, Gwamna Namadi ya jaddada cewa kare tarihi ba wai rubuta shi kadai ba ne, har ma da tabbatar da cewa an rike asali da dabi’u da kuma darussan da ke cikinsa.
Ya ce, “Wannan biki yana tunatar da mu muhimmancin adana tarihi, nazarinsa da kuma yada shi ga al’umma. Ta haka ne za mu kare martabar mu tare da anfani da darussan da suka shafi rayuwar yau da kullum da makoma.”
Gwamnan ya kara da cewa littafin da aka kaddamar da kuma gidan tarihin da aka bude na daga cikin matakan da gwamnati ke dauka domin tabbatar da cewa ilimin tarihi ya kasance a bude ga masu bincike, dalibai da sauran jama’a.
Ya kuma bayyana cewa gwamnati za ta tabbatar da rabon littafin ga daliban makarantu musamman masu nazarin tarihi a matakin sakandare, domin su amfana da ilimin da ke cikinsa.

Gwamna Namadi ya yabawa Sarkin Hadejia bisa kokarinsa na ci gaba da rike al’adun masarautar da kuma tabbatar da dorewar tarihinta, yana mai cewa sarakunan gargajiya na taka muhimmiyar rawa wajen kare tarihi da al’adu.
A karshe, yayin ziyararsa a Hadejia, gwamnan ya halarci wani shirin tallafawa al’umma da sanatan yankin Jigawa ta Arewa maso Gabas ya shirya, wanda ke nuna kudirin gwamnati na hada bunkasa tattalin arziki da kuma kare tarihi da al’adu.
