Gwamnatin Jihar Jigawa tare da ƙungiyar CARE International sun ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarsu domin inganta abinci mai gina jiki da kuma ƙarfafawa Mata gwiwa a faɗin jihar, tare da mai da hankali kan faɗaɗa shirye-shiryen da ke inganta lafiyar uwa da yaro, ƙarfafa wadatar abinci a gidaje, da kuma buɗe damar tattalin arziki ga mata.domin zu dogara da kansu.
An bayyana hakan ne lokacin da a yarin CARE International da shirin CASCADE suka kai ziyarar girmamawa ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, a ranar Alhamis a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin da abokan hulɗar ci gaba ke yi domin duba tasirin ayyukansu tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da gwamnatin jihar.
Da take jawabi yayin ziyarar, Mataimakiyar Darakta ta CARE International a Najeriya, Jennifer Orgle, ta nuna jin daɗinta kan irin goyon bayan da suka samu daga gwamnatin Jigawa, inda ta ce hakan ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarar shirye-shiryensu.
“. Daya daga cikin abubuwan da suka fi bayyana a wannan ziyara shi ne irin goyon bayan gwamnati a duk lokacin aiwatar da ayyukan,” in ji ta.
Ta ƙara da cewa mata da suka amfana da shirye-shiryen sun nuna buƙatar samun ƙarin filayen noma domin su samar da abinci mai gina jiki.
Ta bayyana cewa tawagar ta gana da masu cin gajiyar shirye-shiryen, jami’an gwamnati da kuma ɓangaren masu zaman kansu a sassa daban-daban na jihar, ciki har da ziyarar cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko, inda suka ga gagarumin ci gaba a rayuwar mata da yara.
“Mun ga ci gaba a rayuwar mata da yaransu. Mun kuma ga sauyi mai kyau a rayuwar mutanen da muke aiki da su, kuma mun san cewa ba tare da haɗin gwiwarku ba, da ba za mu iya cimma wannan ba,” in ji ta.
Mrs. Orgle ta jaddada buƙatar faɗaɗa damar samun filayen noma ga mata, musamman masu samar da abinci mai gina jiki, tana mai cewa jami’an gwamnati sun nuna aniyar tallafa wa irin waɗannan shirye-shirye.
A nasa jawabin, Gwamna Namadi ya tarbi tawagar tare da yaba wa CARE International da abokan hulɗarta kan ƙoƙarinsu wajen magance matsalolin rashin wadataccen abinci mai gina jiki a jihar.
Ya bayyana rashin wadataccen abinci mai gina jiki a matsayin babbar matsala ba a Jigawa kaɗai ba har ma a Najeriya baki ɗaya, yana mai jaddada muhimmancin ɗaukar matakai tun da wuri domin tabbatar da makoma mai kyau ga yara.
“Matsalar abinci mai gina jiki babbar matsala ce ba a Jigawa kaɗai ba har ma a Najeriya. Amma ina ganin an yi ƙoƙari sosai tare da tallafin abokan hulɗa da ƙoƙarin gwamnatoci daban-daban. Ina ganin za mu yi nasara, insha Allah,” in ji gwamnan.
Ya kuma bayyana cewa gwamnatinsa ta mayar da hankali sosai kan shirye-shiryen da ke magance matsalar tare da inganta rayuwar jama’a, musamman mata.
Gwamnan ya yi nuni da tasirin shirye-shirye kamar na MASAKI da kuma sabon shirin Tom Brown, wanda aka ƙaddamar domin amfani da albarkatun cikin gida wajen inganta abincin yara.
A cewarsa, an horar da sama da mata 600 a ƙarƙashin shirin, tare da ba su kayan aiki da tallafin farawa, sannan an haɗa su da cibiyoyin kiwon lafiya domin tabbatar da kasuwar kayayyakinsu.
“Mun haɗa kowace mace da wata cibiyar kiwon lafiya domin idan sun samar da kayayyaki, za a samu saye kai tsaye daga ɓangaren lafiya. Da wannan, mun cimma manufofi biyu: muna magance matsalar abinci mai gina jiki, kuma muna ƙarfafa mata,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa ana ci gaba da ƙoƙarin samun amincewar hukumomi kan kayayyakin abinci da ake samarwa a cikin gida, domin tabbatar da inganci da tsaro.
Gwamnan ya tabbatar wa tawagar cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafa wa abokan hulɗar ci gaba, yana mai jaddada cewa irin wannan haɗin gwiwa na da matuƙar muhimmanci wajen inganta rayuwar mata da yara.
Ya ƙara da cewa Jihar Jigawa za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga aiwatar da shirye-shiryen da ke anfani kai tsaye ga al’umma.
