Gwamna Namadi Ya Warware Rikicin Filayen Noma Tsakanin Najeriya da Jamhuriyar Nijar Bayan Shekaru 47, Ya Raba Sabbin Filayen Noma Ga Wadanda Rikicin Ya Shafa
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kawo ƙarshen rikicin filayen noma da ya shafe shekaru 47 yana ci gaba tsakanin al’ummar Jobi da ke Karamar Hukumar Maigatari ta Jihar Jigawa da kuma al’ummar Kyalli da ke Jamhuriyar Nijar, ta hanyar kaddamar da rabon sabbin filayen noma ga manoman da rikicin ya shafa.
An gudanar da bikin ne a Gandun Dajin Dan-Makama, inda aka fara aiwatar da shawarwarin Kwamitin Iyakokin Jihar Jigawa da Hukumar Kula da Iyakokin Kasa ta Najeriya (National Boundary Commission – NBC), lamarin da ya kawo ƙarshen rikicin da ya jima yana kawo cikas ga zaman lafiya tsakanin al’ummomin biyu na kan iyaka.
Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Umar Namadi ya bayyana wannan nasara a matsayin wani babban tarihi ga Jihar Jigawa, yana mai cewa matakin zai dawo da zaman lafiya, haɗin kai da zaman jituwa tsakanin al’ummomin yankin.
“Alhamdulillah. Yau rana ce ta tarihi, domin Allah Ya haɗa mu a wannan wuri domin kawo ƙarshen rashin fahimtar juna da ya daɗe tsakanin al’ummar Jobi ta Karamar Hukumar Maigatari a Jihar Jigawa da kuma al’ummar Kyalli da ke Jamhuriyar Nijar,” in ji Gwamnan.
Gwamnan ya tuna cewa duk da dadadden tarihin zumunci da alakar al’adu tsakanin Najeriya da Jamhuriyar Nijar, batun iyakokin ƙasashe ya haifar da rikicin ne bayan da aka hana manoman Jobi ci gaba da noma a filayen da suka gada kuma suka saba noma a yankin Kyalli.
Ya ce:
“Ko da yake Najeriya da Jamhuriyar Nijar ƙasashe ne ‘yan uwa masu kyakkyawar alaka ta tarihi da al’adu, amma iyakokin ƙasa sun janyo wannan rikici wanda ya ɗauki kusan shekaru arba’in da bakwai.
Mutanen Jobi suna da filayen noma a Kyalli inda suke noma tsawon shekaru. Daga baya aka samu sabani lokacin da mutanen Kyalli suka nuna rashin amincewarsu da ci gaba da amfani da filayen. Hakan ya janyo rikici mai tsawo. Bayan shekaru 47 na rashin jituwa, lokaci ya yi da Allah Ya ƙaddara kawo ƙarshen wannan rikici. A yau, da ikon Allah, an kawo ƙarshensa.”
Gwamna Namadi ya yabawa Hukumar Kula da Iyakokin Kasa ta Najeriya bisa gudummawar da ta bayar wajen sasanta rikicin, yana mai cewa ziyarce-ziyarcen da jami’an hukumar suka rika kai wa Jigawa da shawarwarin ƙwararru da suka bayar sun taka muhimmiyar rawa wajen cimma wannan sulhu.
Ya ce:
“Ina miƙa godiyata ta musamman ga Hukumar Kula da Iyakokin Kasa saboda irin gudummawar da ta bayar wajen warware wannan rikici. Hukumar ta ziyarci Jigawa sau da dama domin nemo mafita. A matsayinsu na ƙwararru kan harkokin iyaka, sun ba gwamnatin jihar shawarwari masu amfani da suka taimaka wajen kawo ƙarshen wannan rikici cikin lumana.”
Har ila yau, Gwamnan ya yabawa Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa kuma Shugaban Kwamitin Iyakokin Jihar, Injiniya Aminu Usman, da sauran mambobin kwamitin, Sarkin Gumel, shugabannin Kananan Hukumomin Maigatari da Sule Tankarkar, sarakunan gargajiya, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki bisa irin haɗin kan da suka bayar wajen samun wannan nasara.
Gwamna Namadi ya kuma jinjinawa al’ummar Jobi da rikicin ya shafa saboda haƙuri, fahimta da amincewarsu da komawa sabbin filayen noma duk da ƙalubalen barin gonakin da suka shafe shekaru suna noma.
Ya ce:
“Babbar godiyarmu ta musamman tana ga mutanen Jobi. A rayuwa, idan mutane sun saba zama ko gudanar da sana’arsu a wani wuri, ba abu ne mai sauƙi a ce su bar wurin ba. Hakan na haifar da damuwa da fargabar rasa hanyar samun abin rayuwa da suka gina tsawon shekaru.”
Tun da farko, Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa kuma Shugaban Kwamitin Iyakokin Jihar, Injiniya Aminu Usman, ya bayyana cewa Gwamna Namadi ne ya kafa kwamitin domin bincike da nemo mafita mai ɗorewa ga rikicin, bayan tattaunawa da Hukumar Kula da Iyakokin Kasa, sarakunan gargajiya, jami’an tsaro da wakilan al’ummomin biyu.
Ya ce kwamitin ya ba da shawarar cewa al’ummar Jobi su daina noma a filayen da ke cikin yankin Kyalli na Jamhuriyar Nijar, yayin da Gwamnatin Jihar Jigawa za ta samar musu da sabbin filayen noma a cikin jihar.
Ya ƙara da cewa:
“Bayan amincewar Gwamna, an ware wani ɓangare na Gandun Dajin Dan-Makama domin noma, sannan aka raba filayen ga mutane 74 da rikicin ya shafa.”
A cikin saƙon fatan alheri daga Babban Daraktan Hukumar Kula da Iyakokin Kasa ta Najeriya, Surveyor Adamu Adaji, wanda Hajiya Yahanasu Aliyu ta wakilta, hukumar ta yabawa Gwamna Umar Namadi bisa amincewa da shawarar samar wa manoman da rikicin ya shafa sabbin filayen noma.
Hukumar ta bayyana matakin a matsayin abin koyi na shugabanci nagari da ke nuna jajircewar gwamnati wajen kare rayuwar al’umma, tare da inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankunan kan iyaka.
